Fara Raba Muhimman Kayayyakin Zabe Da Kone-konen Ofishoshin INEC: Ga Koshi Ga Kwanan Yunwa
A kokarinta na fara shirye-shirye gudanar da zabe da wuri, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa tuni ta raba kashi 50 na kayayyakin zabe.
Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya bayyana haka lokacin da tawaga ta musamman da ke saka ido kan zabe na kungiyar Afirka ta ziyarce shi, inda ya jaddada gwarin gwiwar hukumar na gudanar da sahihin zabe.
Yakubu ya kara da cewa duk da irin kalubalen da hukumar take fuskanta za ta gudanar da sahihin zabe.
Ya ce, “A cikin makonni uku, an kone mana ofishoshi har guda uku a sassa daban-daban na kasar nan. A dukkan wadannan farmaki ba a samu asarar rai ba, amma an kone mana kayayyaki zabe.
“Za dai mu iya dawo da kayayyakin da suka kone, amma ya kamata a dakatar da wannan lamari.
“Ina mai tabbatar da cewa za mu shan ‘yar karamar wahala, amma dai za mu dawo da kayayyakin da muka rasa kuma wannan bai hana hukumar ta gudanar da sahihin zabe kamar yadda doka ta dora mana. Sannan babu gudu babu ja da baya wajen yin amfani da naurar bayyana sakamakon zabe.”
Duk da kiraye-kirayen al’umma na kara wa’adin yin rajistar zabe, amma hukumar da ce hakan zai shafi tsare-tsarenta matukar ta kara wa’adin yin rajista, wanda ta ce tana son kammala duk wasu shiryde-shirye kafin zaben 2023.
Sai dai kuma a wannan makon, shugaban INEC ya fito karara ya bayyana cewa ci gaba da kai hare-hare a ofisoshin INEC babbar barazana ce da ke fuskantar zaben 2023.
Ya dai amince cewa hukumar na iya dawo da wasu muhimman kayayyaki da suka kone amma idan har an dakatar da hare-haren, saboda ci gaba da kone-konen zai iya shafar sababbin kayayyaki da hukumar take rabawa.
Yakubu ya bayyana hakan ne a gaban kwamitin wucin-gadi da ke binciken farmakin kan ofisoshin INEC na majalisar wakilai a Abuja.
Kwamitin ya bayyana rashin jin dadinsa kan yadda ofishin ministan shari’a ke cewa har yanzu bai samu bukata ko guda daya ba na hukunta wadanda suke kai wannan harin.
Yakubu ya ce, “Muna kokarin ci gaba da shirye-shiryenmu na gudanar da zaben 2023. A yanzu dai muna kokarin dawo da dukkan kayayyakinmu ko neman wata hanya ta daban. A halin yanzu dai idan wannan farmaki ya ci gaba da gudana, zai yi wa hukumar wahala da murmure a kan lokaci kafin zaben 2023. Idan har an dakatar da farmakin, to za mu iya murmurewa, amma dai idan har farmakin ya ci gaba da faruwa, zai yi wa hukumar wahala ta murmure. Wannan shi ya sa muke kokarin a dakatar da farmakin wanda ya zama wajibi mu gudanar da wannan sauraron ra’ayi ta yadda za a samu sakamako mai kyau.
“Farmakin ya fara illa ga shirye-shiryen zaben 2023. Abu na farko shi ne, kayayyakin da suka kone musamman ma ofisoshi za su dauki lokaci kafin a iya gyarawa. Su ba kamar bayanai ba ne da za a iya bayarwa daga na’ura. Domin haka, dole a dauki wasu shirye-shiryen na daban. A wasu jihohin da farmakin ya fi zafi, dole mu shirya daukar haya. Ya zama wajibi a wasu wurare mu dauki hayar kayayyaki. A kuma wasu yankunan, ba za mu iya samun hayar kayayyakin ba, wannan ne ta sa dole mu duba wata hanyar kan lalata mana kayayyaki.
“Na biyu, mun rasa kayyaki masu yawa wanda akwai bukatar sake dawo da su. Alal misali a farmakin kwanan nan, mun tafka asarar katinan zabe masu yawa. A kan katin zabe, muna iya dawo da su ta hanyar tura bukata ga babban ofishinmu da ke jiha wajen sake bugawa. Wannan cikin sauki za mu iya dawo da su kuma har a sake bugawa.
“Dole ne hukumar ta ci gaba da hada kai da hukumomin tsaro wajen tsare kayayyakin, kamar yadda na fadi tun a farko akwai matukar kalubale, amma jami’an tsaro za su tsare mu da sauran kayayyakin kasa. Saboda haka, wannan farmaki da ake kai wa ofisoshinmu babban kalubale ne ga jami’an tsaronmu wanda na san za su iya dakatar da shi.