Labarai
Jam’iyyar da ya dace ‘yan Najeriya su zaɓa – Tambuwal
Jam'iyyar da ya dace 'yan Najeriya su zaɓa - Tambuwal
Jam’iyyar da ya dace ‘yan Najeriya su zaɓa – Tambuwal

Jaridar Pemium Times ta tattaro a cikin sanarwan gwamna Tambuwal na cewa jirgin tawagar wakilan ta dira Abeokuta ne domin kai ziyarar girma ga tsohon shugaban kasa, inda ya kara da cewa sun tattauna batutuwa masu amfani.
Gwamna Tambuwal ya kara da cewa:
“Sako na ga yan Najeriya shi ne su fito kwansu da kwarkwata idan ranar zabe ta zo a watan Fabrairu su dangwalawa tikitin da ya hada yan takarar da suka yi dai-dai da al’adar kasar nan, wadanda zasu kafa gwamnatin da zata hada kan kasa.”
“Kuma ta farfado da tattalin arzikin mu kana ta kara dankon zumunci a tsakanin yan kasa, ba kowane tikiti nake nufi ba illa na Atiku Abubakar da gwamana Okowa.”